👇👇👇👇👇👇

1) Ka Kama Hanyar Allah Kyam ko

da za ka yi asarar duk Duniyar

nan ne.


2) Ka Sadaukar da Kanka da

Dukiyarka ga Wannan Harka ta

Tajdidin Musulunci.


3) Ka yi wa Kanka Tarbiyya ta

Yadda za ka Siffantu da Siffofin

Addinin a Zantukanka da

Ayyukanka.


4) Ka Himmatu Wajan Neman

Ilimin Addini da Aiki da Shi.


5) Ka Guji Zaman Jagwab, ka

Nemi Sana'ar da za ka yi.


6) Ka ji Tsoron Yawo da Tsegumi,

ka Kuma Kwabi mai yin Hakan.


7) Kar ka Sanya Kanka cikin

Rigingimun Mazhabobi, abin da

ya Hada mu yafi Karfin Mazhaba.


Rawani abin Girmamawa ne,

in ka sa ka Alamtu da Addini a

Zantukanka da Ayyukanka.


9) Kar mu Ba Da'awarmu Wata

Sura ta Cewa mu Siyasa ce ta

dame mu.


10) Lalle ne Da'awarmu ta zama

tana Dauki dai-dai ne, Ba ta jawo

Mutane duuuu ba.


11) Ya Kamata Da'irori su Rika

Tsirowa ne, Amma ba a Rika Kafa

su ba Kamar na "Yan Wa'azin

Kasa baki daya.


12) Ya Zama ka Shiga Wannan

Harkar ne Domin ka Tsamar da

Kanka Daga Fushin Allah Ranar

Gobe Kiyama.

-

-

Domin Samun Cikakkiyar

Fahimtar Wadannan Nasihohin

ka Nemi Jawaban Sayyeed [H] na

Ijtima'o'in Kano da Zariya.